Labarai

Annobar tsintsaye ta Sauka a faransa

Spread the love

Jama’ar Faransa da ke daya daga cikin kasashen Turai da Corona ta tagayyara sun firgita sakamakon samun bullar murar tsuntsaye a gari na biyu a kasar.

Ma’aikatar Noma da Kiwo ta rawaito sanarwar da Ofishin Tsare Lafiyar Jama’a ya fitar inda aka fadi cewar an kashe dubunnan daruruwan kaji sakamakon kamuwa da murar tsuntsaye a garin Yvelines baya ga Tsibirin Korsika.

Sanarwar ta ce, kwararru na gudanar da binciken gano alakar bullar cutar a garuruwan biyu daban.

A gefe guda kuma, gwamnati ta fara daukar matakan hana cutar kama wasu dabbobin na daban.

A farkon watan Nuwamba ne Faransa ta killace dabbobin da ake kiwo a gida sakamakon yadda tsuntsaye masu gudun hijira suka sauya hanyarsu tare da bi ta cikin kasar Faransa.

A kasuwannin kasar kuma an hana sayar da tsuntsayen gida da na daji, LABARAI 24

Related Articles

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

Back to top button